Samurah bn Jundub (r.a) ya ce: Wata rana Manzon Allah (s.a.w) ya bamu labari, ya ce; Lallai jiya da dare wasu su biyu sun zo min, sai suka tashe ni, sannan suka ce da ni; mu tafi, sai na tafi tare da su. 1. Sai muka izo wani mutum a kwance, ga wani kuma a tsaye a kansa riƙe da 🪨 dutse, sai ya ɗauki wannan dutsen ya rotsa kan na kwancen har sai kansa ya fashe, dutsen ya yi gefe, idan ya tafi ɗauko dutsen kafin ya dawo, kan ya sake haɗewa, sannan ya sake rotsa masa dutsen a kansa! Sai na ce musu; Subhanallahi, su waye waɗannan kuma? Sai suka ce min; mu tafi, mu tafi, sai muka tafi. 2. Sai muka iso wani mutum yana kwance kan ƙeyarsa, ga wani kuma a tsaye a kansa riƙe da 🪝 ƙugiya na baƙin ƙarfe, sai ya zo gefen bakinsa ya sanya ƙugiyar nan, ya tsaga bakinsa har sai ƙugiyar ta fito ta ƙeyarsa, sannan ya sanya ƙugiyar a ƙofar hancinsa na gefe ɗaya, har sai ya huda ta fito ta ƙeyarsa, sannan ya saka ƙugiyar ta idonsa ɗaya, ya huda har sai ta fito ta ƙeyarsa, sannan ya cire ƙugiyar ya koma ɗ...